Daga Usman Dahiru, Bauchi
Rikicin siyasa da ke faruwa a cikin Jam’iyyar APC a Jihar Bauchi ya dauki sabon salo mai tayar da hankali, inda tsohon gwamnan jihar, Isa Yuguda, ya koma yin manyan zarge-zarge kan Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar.
Amma idan aka cire hayaniyar, tambaya mafi muhimmancin ita ce: shin wadannan zarge-zarge suna da hujjoji ne ko kuwa wani shiri ne na siyasa domin raunana wanda ake gani a matsayin abokin hamayya?
Idan aka yi nazari a kan wadannan zarge-zarge, za a ga irin tsarin da aka saba gani a siyasar Najeriya—manyan zarge-zarge da ake yi ba tare da gabatar da hujja a fili ba.
Zargin cin hanci, haddasa rikici da kuma kokarin lalata jam’iyya abubuwa ne masu nauyi da ke bukatar hujja, ba sanarwar manema labarai ba. I
dan babu hujja, ana iya kallon su a matsayin dabarun siyasa domin bata sunan Tuggar wanda ke kara tasiri a cikin APC.
Haka kuma yana da muhimmanci a lura cewa Yusuf Tuggar ba sabon ɗan siyasa ba ne. Kafin nada shi Ministan Harkokin Waje, ya taba zama dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gamawa a Jihar Bauchi.
A lokacin da yake majalisa, an san shi da gudunmawarsa a muhawara, tsare-tsaren manufofi da kuma ayyukan raya mazabarsa, wanda ya ba shi suna a matsayin ɗan majalisa mai himma da kwarewa.
Bayan aikinsa na majalisa, Tuggar ya ci gaba da zama mai tasiri a cikin APC, inda ya taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasa na jam’iyya da kuma matakin kasa baki daya.
Yana daga cikin mutanen da suka taka rawar gani wajen nasarar da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben da ya gabata, ta hanyar hada kai, tsara dabaru da kuma karfafa gwiwar magoya baya a wurare masu muhimmanci.
Yusuf Tuggar, a matsayinsa na Ministan Harkokin Waje na Najeriya, yana rike da mukami mai nauyi da ke bukatar hulda da kasashen duniya da wakiltar kasa.
Saboda haka, yana da wuya a gaskata cewa minista mai irin wannan nauyi zai bar aikinsa ya koma haddasa rikicin cikin gida na jam’iyya a matakin jiha.
Irin wadannan zarge-zarge ba kawai suna tauye martabarsa ba ne, har ma suna rage darajar tattaunawar siyasa.Abin da ya fi yiwuwa shi ne yadda tasirin Tuggar a siyasar Bauchi ke kara fitowa fili yana damun wasu masu ruwa da tsaki.
Tarihi ya nuna cewa a irin wannan lokaci, zarge-zarge kan zama makamin siyasa—ba don sanar da jama’a gaskiya ba, sai dai domin karkatar da ra’ayi da sarrafa yanayin siyasa.Abin da ya fi tayar da hankali shi ne yadda ake kokarin mayar da sha’awar siyasa kamar laifi.
A tsarin dimokuraɗiyya, neman mukami abu ne na al’ada kuma halal. Matsalar ita ce kokarin dakile wannan sha’awa ta hanyar zarge-zarge marasa hujja da bata suna.Idan da gaske akwai zargi mai tushe, hanya a bayyane take—gabatar da hujja ga jam’iyya ko hukumomin doka.
Amma kai zarge-zarge a kafafen yada labarai ba tare da hujja ba yana kara raba kai da rage amincewar jama’a.A lokacin da APC a Bauchi ya kamata ta kara karfi da hadin kai, sai aka karkata zuwa rikicin cikin gida.
Wannan ba kawai ba shi da anfani ba ne, har ma yana iya bai wa jam’iyyun adawa damar cin moriya
.A bangarensa, Tuggar ya mayar da hankali kan aikinsa na kasa ba tare da shiga rikice-rikicen siyasa na cikin gida ba. Wannan hali na nuna kwarewa da kamun kai wanda ya kamata a yaba masa.
A karshe, APC a Bauchi dole ta yanke shawara—shin tana son ci gaba ne ko kuma rikici? Sabani na siyasa abu ne na al’ada, amma amfani da zarge-zarge marasa hujja hanya ce mai hatsari.
A ƙarshe, auna shugabanci ba da yawan zarge-zarge ake yi ba ne, sai dai da iya hada kai da gina juna.
Har sai an yi hakan, ‘yan Najeriya za su ci gaba da tambaya: wa ke cin moriyar wannan rikici a APC ta Bauchi?
Baya ga wadannan zarge-zarge na yanzu, yana da muhimmanci a tuna da wasu abubuwa da suka shafi mulkin Isa Yuguda a baya.
Rahotanni daga baya sun danganta gwamnatinsa da binciken hukumomin yaki da cin hanci, wanda ya bar tambayoyi a zukatan jama’a.
A wani rahoto da ya shahara, hukumar EFCC ta rufe wata kadarar da ake dangantawa da Isa Yuguda a Bauchi, a matsayin wani bangare na binciken zargin amfani da mukami ba daidai ba da kuma karkatar da kudaden gwamnati.
Haka kuma, an taba samun rahotanni da ke nuna cewa EFCC ta binciki wasu kadarori da harkokin kudade da ake dangantawa da shi, wanda ya kara jawo hankalin jama’a kan yadda aka tafiyar da mulkinsa.
Hakazalika, wani kwamitin bincike da aka kafa daga baya ya gano wasu kura-kurai a harkokin kwangila tsakanin 2007 zuwa 2015, inda aka ce an kasa bayyana yadda aka kashe wasu biliyoyin naira.
Duk da cewa zargi ba hujja ba ne, amma yana cikin tarihin jama’a. Saboda haka ya zama dole masu yin zarge-zarge su nuna kame kai.
Dangane da haka, akwai bukatar Isa Yuguda ya fito ya bayyana matsayinsa kan wadannan batutuwa. Yin shiru na kara haifar da tambayoyi.
Masu lura da al’amura suna ganin cewa duk wanda ya taba fuskantar irin wadannan zarge-zarge ya kamata ya yi taka-tsantsan wajen zargin wasu.
Dangane da haka, akwai bukatar ya amsa tambayoyi kamar:
1. Mene ne matsayinka kan zarge-zargen cin hanci da suka biyo bayan mulkinka?
2. Mene ne sakamakon binciken EFCC kan kadarorinka?
3. Ta yaya kake mayar da martani kan zargin rashin daidaito a harkokin kuɗi?
4. Wane irin gagarumin aiki ka bari a Bauchi?
5. A wane matsayi kake ganin kana da ikon zargin wasu?
Saboda haka, wasu na ganin ya kamata ya fara warware wadannan tambayoyi kafin alakanta kansa da jam’iyya mai daraja irin APC.
A makonnin baya, an kuma nuna damuwa kan rawar da ɗansa, Muslim Isa Yuguda, ke takawa a cikin rikicin APC a Bauchi. Ana zargin cewa yadda yake shiga harkokin jam’iyya na iya kara raba kai.
Masana na ganin cewa sabbin ‘yan siyasa ya kamata su hada kai, amma irin wadannan zarge-zarge na jawo tambayoyi kan tasirin hakan ga jam’iyyar APC a Bauchi.


